Ran maza ya baci: Ku kama mawakin da ya ci zarafin dan sandanmu ku kai shi Kotu, IGP ya yi umarni


Babban Sufeto Janar na ‘Yan Sandan Najeriya (IGP), Usman Alkali Baba ya bayar da umarnin a kamo mawakin nan na Afrobeat, Seun Kuti bisa laifin cin zarafin dan sanda.

 IGP, a wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar, CSP Olumuyiwa Adejobi ya fitar a ranar Asabar, ya umarci kwamishinan ‘yan sandan jihar Legas da ya kama Kuti. PM News ya rahoto.

 An ce an dauki Kuti a faifan bidiyo yana cin zarafin wani dan sanda sanye da kayan aiki.

 “IGP din ya kuma ba da umarnin gudanar da bincike cikin gaggawa kan musabbabin harin da kuma gurfanar da wanda ake tuhuma a kan haka.

 “IGP Usman Alkali Baba ya tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa ba za a amince da ayyukan raina ko kyama ga alamomin hukuma ba, yayin da za a gurfanar da masu aikata manyan laifuka,” in ji shi.

 An nuna Seun Kuti a cikin wani faifan bidiyo yana marin wani dan sanda sanye da kayan aiki

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN