Type Here to Get Search Results !

Main event

Kayya jama'a: Malamin Islama ya taushe dalibarsa yar shekara 6 ya yi lalata da ita a cikin wani aji a makarantar Al'quran da yake karantarwa


An gurfanar da wani malamin addinin Islama, Mosediq Toheeb, mai shekaru 24, a gaban wata kotun Majistare ta Yaba a birnin Lagos bisa zargin yin lalata da wata daliba mai shekaru shida a makarantar Alkur’ani da yake koyarwa.

 An gurfanar da wanda ake zargin ne a gaban kuliya bisa laifuka biyu na cin zarafi da hukumar ‘yan sandan jihar ta yi masa.  Dan sanda mai shigar da kara, Thomas Nurudeen, ya shaida wa kotun cewa lamarin ya faru ne a ranar 7 ga watan Mayu, 2023, a babban masallacin jami’ar Legas.

 Rahotanni sun bayyana cewa, wannan ne karo na biyu da ake zargin malamin ya yi lalata yarinyar.  An gano lamarin ne bayan da yarinyar ta dawo gida daga makaranta da tabon jini a tufafinta.  Ta gaya wa mahaifiyarta cewa malamin aji ya kai ta wani aji daban, ya É—aure mata baki da hannu ya Æ™azantar da ita tare da gargaÉ—in cewa kada ta gaya wa kowa.

 Lauyan mai gabatar da kara ya ce laifukan da aka aikata suna da hukunci a karkashin sashe na 261 da 137 na dokokin laifuffuka na jihar Legas 2015. Laifin da ake tuhumarsa da shi ya ce;

 Yayin da Nurudeen ya roki kotun da ta ci gaba da tsare wanda ake kara na tsawon kwanaki 30 har zuwa lokacin da za a ba da shawarar lauyoyi daga sashin kula da kararrakin jama’a, lauyan Toheeb, Patrick Onochie, ya roki kotun da ta duba wanda ake kara wanda ya ce dalibi ne na ajin karshe a jami’ar Legas kuma  zai fara jarrabawar karshe nan da makonni biyu.

 Alkalin kotun mai shari’a Nwaka wanda bai amsa rokon wanda ake tuhuma ba, ya bayar da umarnin a ci gaba da tsare shi.  Alkalin kotun ya ce babu wata takarda da ke gaban kotun da ta nuna wanda ake tuhumar dalibi ne kuma a shekararsa ta karshe ko kuma zai fara jarrabawa.

 Kafin ya dage ci gaba da sauraron karar har zuwa ranar 19 ga watan Yunin 2023, alkalin kotun, Nwake ya bayar da umarnin a sake kwafin karar tare da aika wa daraktan kararrakin jama’a na jihar Lagos domin neman shawarar shari’a.

Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN

Hollywood Movies