Type Here to Get Search Results !

Daga Karshe, Asalin Dalilin da Ya Sa Bola Tinubu Ya Gana da Kwankwaso a Faransa Ya Bayyana


Zababben ɗan majalisar wakilan tarayya, Honorabul Abdulmumini Jibrin, ya yi ƙarin haske kan ganawar zababben shugaban kasa, Bola Tinubu, da Rabiu Kwankwaso a Faransa.

Jaridar The Nation ta rahoto cewa Tinubu ya gana da Kwankwaso, ɗan takarar shugaban ƙasa a inuwar NNPP a zaben 2023 ranar Litinin 15 ga watan Mayu, 2023 a ƙasar Faransa.

A cewar Jibirin, shugaban ƙasa mai jiran gado ya zauna da Kwankwaso ne a kokrain ganin ya inganta haɗin kan ƙasa, fahimtar juna da kuma kawo ci gaba.

Meyasa manyan 'yan siyasan suka sa labule a Faransa?

Ɗan majalisar tarayyan ya ƙara da bayanin cewa a iya saninsa, Tinubu ba zai yi watsi da mutanen da suka taimake shi a lokacin babban zaben da ya gabata ba, kamar yadda Channels tv ta rahoto.

Jibirin ya yi wannan ƙarin haske domin kawo karshen kace-nace kan lamarin a wani sakon murya da ya fitar ranar Lahadi, 21 ga watan Mayu, 2023.

ÆŠan majalisar ya ce:

"Bana tunanin Tinubu zai yi watsi da waɗanda suka taimake shi lokacin zaɓe, amma yana da burin gina haɗin kan ƙasa, fahimtar juna da kawo ci gaba."

Haka nan kuma, kalaman Jibrin sun yi Alla-wadai da wani sautin murya, wanda aka ji gwamnnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya nuna rashin jin daÉ—insa da lamarin.

Honorabul Jibrin ya yi bayanin cewa gabanin Tinubu ya sa labule da Kwankwaso, sai da ya tuntuɓi gwamna Ganduje na jihar Kano.

Ya ce Gwamna Ganduje da tsohon gwamnan Kano kuma jagoran NNPP na ƙasa zasu iya sasanta duk wani saɓani da ya shiga tsakaninsu.

Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN