Type Here to Get Search Results !

Yadda ake zargin soji sun yi wa Manajan KEDCO, jami'an wutan lantarki, Kwastomomi duka a Kebbi


Rahotanni daga garin Birnin kebbi a jihar Kebbi na cewa ana zargin jami'an soji sun yi wa jama'a duka a ofishin KEDCO da ke GRA Nepa a garin Birnin kebbi. Shafin labarai na isyaku.com ya samo. 

Lamarin ya faru ne da misalin karfe 1:30 na ranar Asabar 29 ga watan Afrilu. Gaddafi Ibrahim, Manajan KEDCO na jihar Kebbi, a wani faifen bidiyo, ya ce jami'an sun shigo harabar KEDCO inda suka yi wa wasu bayin Allah duka

Ya ce wadanda lamarin ya shafa sun hada da shi kansa inda ya sami targade a hannu, sai kuma jami'an tsaro Black Tiger Security da ke tsaron harabar maaikatar duk an yi masu duka.

Ya kara da cewa lamarin ya rutsa da kwastomomi da suka je KEDCO don su biya kudin wuta, cikinsu har da wani Alakali.

Ba wani tabbaci, ko  bayani da shafin labarai na yanar gizo isyaku.com ya samu daga barikin soji na Birnin kebbi kan lamarin. Kazalika wata majiya ta bukaci wakilin isyaku.com ya tuntubi ofishin soji ranar Litinin don tantance zargin.

Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN