Type Here to Get Search Results !

Kuma dai: Hisbah ta tsinto jarirai biyu da aka yar da su a bola a jihar Kebbi


An tsinci jarirai biyu da ransu bayan an haife su kuma aka yar da su a wurare daban daban a jihar Kebbi.

Lamarin ya faru ne a mako na farko.kafin shigowar watan Ramadana. Shafin labarai na yanar gizo isyaku.com ya ruwaito

Kwamandan Hisbah na jihar Kebbi Ustaz Sulaiman Muhammad ya sanar wa manema lamarai ranar Talata 25 ga watan Afrilu 2023 a garin Birnin kebbi.

Ya ce an tsinci jariri na farko an yar da shi a bola a Unguwar Badariya a garin Birnin kebbi.

Yayin da aka tsinci jariri na biyu a garin Ambursa. Ya ce duk jariran na raye lokacin da aka tsincesu, kuma ana kula da su a gidan Marayu a garin Birnin kebbi.

Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN