Hadimin Atiku Ya Yi Hasashen Mutum 20 da Bola Tinubu Zai Ba Mukamai a Gwamnatin sa


Daniel Bwala wanda Mai magana da yawun bakin Atiku Abubakar ne a zaben 2023, ya yi hasashen yadda Gwamnatin mai zuwa za ta kasance. 

A ranar Juma’a, Daniel Bwala ya rika jero wasu ‘yan siyasa da kuma mukaman da yake ganin za su samu idan Bola Ahmed Tinubu ya hau karagar mulki. Legit ya wallafa.

Tsohon jagoran na jam’iyyar APC mai mulki ya yi hasashen wadanda za su zama Ministoci, Hadiman shugaban Najeriya da kuma shugabannin majalisa.

Kamar yadda Vanguard ta bibiyi ‘dan siyasar a shafinsa, ga yadda ya yi hasashen na shi:

Jerin shugabannin gobe

Shugaban kasa - Bola Ahmed Tinubu

Mataimakin shugaban kasa - Kashim Shetima

Shugaban majalisar dattawa - Godswill Akpabio

Shugaban ma’aikatan fada - Femi Gbajabiamila

Mai bada shawara kan tsaro - Nuhu Ribadu

Hadimin harkar cikin gida - Babajimi Benson

Sakataren gwamnatin kasa - Nasir El-Rufai

Mai magana da yawu - Festus Kayamo

Ministan harkar musamman - James Faleke

Ministan birinin Abuja - Yahaya Bello

Ministan tsaro - Tukur Buratai

Ministan yada labarai - Bayo Ononuga

Ministan harkokin waje - Kayode Fayemi

Ministan cikin gida - Nyesom Wike

Ministan shari’a (AGF) - Babatunde Fashola

Ministan harkar noma - Ben Ayade

Ministan jiragen sama - Femi Fani Kayode

Ministan ayyuka - Ken Nnamani

Lauyan gidan gwamnati - Babatunde Ogala

Rahoton Daily Post ya nuna Bwala ya hango Dele Alake a kujerar Jakadan Najeriya a Amurka, amma bai san shugaban majalisar wakilai ba.

A cewarsa, Buba Marwa zai cigaba da rike NDLEA, sai Wale Edun ya zama Gwamnan babban banki, ya yi gum a kan kujerun EFCC, DSS da NIA.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN