Babbar magana: Wike ya yi wa masaukin zababben shugaban kasa Tinubu dirar bazata a Abuja, dalilai sun bayyana


Gwamnan jiha Rivers Nyesom Wike a ranar Juma'a ya kai  ziyarta ga zababben shugaban kasa, Asiwaju Bola Tinubu
.

 Tinubu na zaune ne a wani gida da aka ware masa gabanin rantsar da shi a matsayin shugaban Najeriya ranar 29 ga Mayu, 2023. PM News ya rahoto.

 Kalli bidiyo a kasa:

 Wike ya dira Abuja a ziyarar tare da takwaransa na jihar Oyo, Seyi Makinde.

 Ya yi kira da a marawa Tinubu baya domin ganin gwamnatinsa ta samu nasara.

 A cewarsa an yi zabe kuma ya yi nasara, yana mai cewa ya zama wajibi dukkan ‘yan Najeriya su ba shi goyon bayan da ya dace domin amfanin ‘yan Najeriya.

 Gwamnan ya ce lokacin siyasa ya wuce, ya kara da cewa yana da yakinin cewa Tinubu na da abin da ya kamata ya yi wa Najeriya.

 Wike ya yi aiki tukuru don fitowar Tinubu a matsayin zababben shugaban kasa yayin da ya kai masa kuri’un Rivers.

 Haka kuma, Makinde ya tabbatar da cewa Tinubu ya yi nasara sosai a jihar Oyo yayin zaben shugaban kasa da aka gudanar a ranar 25 ga watan Fabrairu.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN