Type Here to Get Search Results !

Main event

APC ta kori zababben sanata kwanaki kadan bayan ya lashe zabe, duba dalili


Rikicin cikin gida a jam’iyyar APC na ci gaba da habaka yayin da a karshen makon nan jam’iyyar ta kori zababben sanata David Jimkuta a karshen makon nan.

Ofishin jam’iyyar APC na karamar hukumar Takum ce ta dakatar da sabon sanatan bisa zarginsa da cin dunduniyarta. Legit ya wallafa.

Dakatar da sanatan na kunshe ne a cikin wata mudawwari mau dauke da sa hannun shugabanni 21 cikin 27 na kananan hukumomin jihar, rahoton jaridar Punch.

A cewar shugaban APC na yankin, Hon, Sirajo Sallau a cikin sanarwar mai dauke da kwanan watan 7 ga watan Afrilu, an dakatar da sanatan ne biyo bayan duba cikin tsanaki.

A cewarsa, kwamitin da aka hada don bincike kan ayyukan sanatan ne ya yanke hukuncin dakatar da sanatan a matsayin matakin farko na ladabtarwa, rahoton Sahara Reporters.

Martanin zababben sanatan bayan sanar da korarsa
A lokacin da aka tuntube shi, David Jimbuta ya ce:

“Wadanda suka sanya hannu kan takardar korar mara tushe ba mambobin jam’iyyar bane. Don haka, ban damu ba."
Rahotanni a baya sun bayyana cewa, akwai kitimurmura a game da kujera da tikitin sanatan Taraba ta Kudu a APC tsakanin zababben sanatan da kuma Usman Danjuma Shiddi.

Jimkuta ya maka Shiddi a kotu game da sakamakon zaben fidda gwanin da aka yi, inda daga baya ya yi nasara.

An dakatar da Amos ne a daidai lokacin da ake ci gaba da shirin rantsar da zababbun ‘yan siyasan da suka yi nasara a zaben bana.

Ya zuwa yanzu, jam’iyyar APC ta bayyana dalilin dakatar da sanatan tare da bayyana yadda ya gaza kare kansa a gaban wani kwamiti.

Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN

Hollywood Movies