Yar jarida mai shekara 26 ta ci zaben dan Majalisar Kwara


Wata matashiya mai shekara 26, Rukayat Motunrayo Shittu, ta zama zababbiyar 'yar Majalisar Dokokin Jihar Kwara. Rahotun Jaridar Aminiya. 

Zababbiyar 'yar matashiyar ta kasance 'yar jarida, kafin ta tsunduma harkar siyasa.

Rukayat ta Jam'iyyar APC ta yi nasara ne bayan ta lallasa abokin karawarta, Abdullah Magaji, na jam'iyyar PDP.

Baturen zaben, Farfesa Akeem Olasunkanmi Ijaiya, ya sanar cewa Rukayat Motunrayo Shittu, ta yi nasara ne bayan da ta samu kuri'u 7,521, shi kuma Abdullah Magaji na PDP ya samu 6,957.

A halin yanzu Rukayat, za ta kasance mafi karancin shekaru a cikin 'yan majalisar dokokin jihar.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN