Kai tsaye: An kirga sakamakon zaben Gwamna a kananan hukumomi 6 cikin 21 a jihar Kebbi


Hukumar zabe mai zaman kanta a jihar Kebbi INEC ta fara kudayar sakamakon kuri'un zaben Gwamna da na Majalisar dokoki da aka gudanar a jihar.

Gidan rediyon tarayya Equity FM Birnin kebbi ta labarta cewa an kammala kidayar kuri'un shida daga cikin kananan hukumomi 21 da ke fadin jihar.

Kananan hukumomin sun hada da Aliero, Bunza, Kalgo, Maiyama, Suru da Zuru. Equity FM ta ce dan Takarar jam'iyar APC ke kan gaba a kananan hukumomi hudu cikin shida kawo yanzu.

Yayin da na jam'iyar PDP la lashe kananan hukumomi biyu cikin shida kawo yanzu.

Ana ci gaba da tattara tare da kidayar kuri'un sauran kananan hukumomi. 

Ku kasance da mu don kawo maku sakamakon sauran kananan hukumomi da zarar INEC ta kammala kidayar....

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN