Yan daba sun kashe mutum, sun jikkata wasu a wurin zabe


Mutum daya ya rasu, wasu da dama sun samu raunuka bayan ’yan daba sun kai farmaki a rumufunan zabe a sassan Jihar Legas. Jaridar Aminiya ta ruwaito.

Aminiya ta gano cewa an harbe mutum daya har lahira, wasu da dama kuma sun jikkata a lokacin da bata-garin suka yi dirar mikiya a wuraren zaben.

Yankunan da aka kai hare-haren sun hada da Ikota, Jakande, Ijegun, Festac da kuma Isolo.

Rikicin ya fara barkewa ne bayan bata-garin sun kutsa cikin yankin Okota, inda jam’iyyar LP ke da karfi.

Maharan sun fatattaku mutanen da suka fito yin zabe, sannan suka lalata akwatunan zabe, suka tafi da wasu.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN