An harbe mutum daya har Lahira a yayin zanga-zangar Kenya


An harbe mutum daya har lahira a birnin Kisumu da ke yammacin kasar Kenya yayin da masu zanga-zanga suka fito domin nuna adawa da tsadar rayuwa. BBC ya ruwaito.

 An kuma yi arangama tsakanin masu zanga-zanga da 'yan sanda a wasu matsugunan da ba na yau da kullun ba a birnin Nairobi.

 Gwamnati dai ta tura jami'an tsaro domin dakile zanga-zangar da madugun 'yan adawa Raila Odinga ya kira, amma hakan ya kara ruruta wutar rikici.

 Ma'aikatar harkokin cikin gida da kuma sufeto janar na 'yan sanda sun bayyana zanga-zangar a matsayin haramtacciya.

 A halin yanzu dai shugaba William Ruto yana wata ziyarar aiki a kasashen Belgium da Jamus.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN