Type Here to Get Search Results !

An harbe mutum daya har Lahira a yayin zanga-zangar Kenya


An harbe mutum daya har lahira a birnin Kisumu da ke yammacin kasar Kenya yayin da masu zanga-zanga suka fito domin nuna adawa da tsadar rayuwa. BBC ya ruwaito.

 An kuma yi arangama tsakanin masu zanga-zanga da 'yan sanda a wasu matsugunan da ba na yau da kullun ba a birnin Nairobi.

 Gwamnati dai ta tura jami'an tsaro domin dakile zanga-zangar da madugun 'yan adawa Raila Odinga ya kira, amma hakan ya kara ruruta wutar rikici.

 Ma'aikatar harkokin cikin gida da kuma sufeto janar na 'yan sanda sun bayyana zanga-zangar a matsayin haramtacciya.

 A halin yanzu dai shugaba William Ruto yana wata ziyarar aiki a kasashen Belgium da Jamus.

Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN