Sudan ta fara tattaunawa domin hada bangarorin soji wuri guda


Shugabannin siyasa na soji da na farar hula a Sudan sun fara tattaunawa a birnin Khartoum kan mayar da mayakan da ke samun goyon bayan gwamnati RSF karkashin rundunar soji.

 Wannan, da sanya sojoji a karkashin ikon farar hula, sune muhimman bukatun kungiyoyin farar hula wadanda suka taimaka wajen hambarar da shugaba Omar al-Bashir a shekarar 2019. BBC ta ruwaito.

 Tattaunawar ta ranar Lahadi wani bangare ne na yarjejeniyar da aka rattabawa hannu a cikin watan Disamba, da nufin share fagen komawa kan tafarkin dimokuradiyya, wanda kuma ya kamata a amince da shi a hukumance cikin kasa da makonni biyu.

 Babban hafsan sojin kasar Abdel Fattah al-Burhan wanda ya kwace mulki a wani juyin mulki shekaru biyu da suka gabata ya ce yana son kawo karshen sojojin da ke goyon bayan gwamnatocin kama-karya a Sudan.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN