Type Here to Get Search Results !

Main event

Sudan ta fara tattaunawa domin hada bangarorin soji wuri guda


Shugabannin siyasa na soji da na farar hula a Sudan sun fara tattaunawa a birnin Khartoum kan mayar da mayakan da ke samun goyon bayan gwamnati RSF karkashin rundunar soji.

 Wannan, da sanya sojoji a karkashin ikon farar hula, sune muhimman bukatun kungiyoyin farar hula wadanda suka taimaka wajen hambarar da shugaba Omar al-Bashir a shekarar 2019. BBC ta ruwaito.

 Tattaunawar ta ranar Lahadi wani bangare ne na yarjejeniyar da aka rattabawa hannu a cikin watan Disamba, da nufin share fagen komawa kan tafarkin dimokuradiyya, wanda kuma ya kamata a amince da shi a hukumance cikin kasa da makonni biyu.

 Babban hafsan sojin kasar Abdel Fattah al-Burhan wanda ya kwace mulki a wani juyin mulki shekaru biyu da suka gabata ya ce yana son kawo karshen sojojin da ke goyon bayan gwamnatocin kama-karya a Sudan.

Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN

Hollywood Movies