Type Here to Get Search Results !

Abin da ya sa INEC ta ce zaben Gwamnan jihar Kebbi bai kammala ba


Hukumar zabe mai zaman kanta a jihar Kebbi INEC ta ce ba a kammala zaben Gwamna da aka yi ba na ranar Asabar. 

Jami'in tattara sakamakon zaben Farsefa Ysusuf Sa'idu na Jami'ar Usman Dan Fodio Sokoto, ya ce an sami kuri'u fiye da yawan kuri'u da aka yi rijista kafin zaben. Equity FM Birnin kebbi ya labarta.

Ya ce dan takarar jam'iyar APC Nasir Idris ya sami kuri'u 388,258 yayin da dan takarar PDP Aminu Bande ya sami kuri'u 342,980. Dan takarar jam'iyar PRP Udu Idris ya sami kuri'u 3103.

Ya ce an soke zabuka a wasu mazabu a kananan hukumomi 20 cikin 21 a fadin jihar Kebbi.

Ya ce hakan na kunshe ne a sashe na 51 (2-3) na dokar zabe da ya ce "Idan yawan kuri'u da aka kada sun zarce yawan kuri'u da aka yi rijista a rufnar zabe. Za a soke sakamakon zabe har sai an gudanar da sabon zabe kafin a fadi sakamako".

Farfesa ya ce dokar zabe ta bayar da damar a sake gudanar da zabe a wuraten da aka sami aringizon yawan adadin masu kada kuri'a kafin a fadi sakamakon zabe. 

Post a Comment

1 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.
  1. Allah yazabamuna abinda yfi zama Alkhari

    ReplyDelete

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN