Type Here to Get Search Results !

Yanzu yanzu: An kashe wani matashi bayan yan daba sun farmaki rumfar zabe ana kada kuri'u a jihar Kogi


Rahotanni daga jihar Kogi na cewa wani matashi mai suna Akayama a yankin Anyigba da ke kamaramar hukumar Dekina ya mutu bayan yan bindiga sun bindige shi
.

Wau yan daba da suka farmaki garin don sace kayan zabe ne suka bindige matashin har lahira, jaridar Daily Trust ta rahoto.

Lamarin ya afku ne da misalin karfe 11:00 na safiyar yau Asabar, 25 ga watan Fabrairu inda ake gudanar da zaben shugaban kasa a fadin kasar. Legit Hausa ya wallafa.

Yan daban sun mamaye garin suna ta harbi kan mai uwa da wahabi sannan suka dungi sace kayan zabe daga mazabu daban-daban.

An harbe maarigayin wanda mazauna yankin suka yi ikirarin cewa ya kammala karatunsa a bangaren ilimin tattalin arziki a jami'ar Prince Abubakar Audu, Anyigba, a wata rumfar zabe da ke in Iji-Anyigba.

Lamarin ya hargitsa zaben da ke gudana a garuruwan Dekina, Agbeji, Ajiolo, Abejukolo da Ejule yayin da yan daba suka kwace rumfunar zabe, suna kora masu zaben da basa biyayya ga wata jam'iyya.

A halin yanzu, an ce an tura sojoji domin su dawo da zaman lafiya a yankin.
INEC ta soke zabe a rumfunar zabe 7 a yankin Kogi ta gabas
A halin da ake ciki, jaridar Vanguard ta rahoto cewa an soke tsarin zabe a rumfunar zabe bakwai a yankin Kogi ta gabas.

Yayin da aka soke zabe a rumfunar zabe biyu a Anyigba, karamar hukumar Dekina, sauran rumfuna biyar da aka soke zaben sun kasance a yankin Omala ta jihar Kogi.

Daya daga cikin rumfar da aka soke ita ce rumfar 01, gudunmar Abejukoli da ke karamar hukumar Omala.

Post a Comment

3 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.
  1. To Allah ya jikansa ya sa a gama zabe lafiya

    ReplyDelete
  2. Wai yandaba su kashe mutum a wajen zabe Kuma jami'an tsaro basu kamasu ba

    ReplyDelete
  3. Ko ku kashekowa dakowa Atiku ne sugabankasa

    ReplyDelete

Rubuta ra ayin ka

Top Post Ad

Below Post Ad

Hollywood Movies