Yan sandan jihar Kebbi sun cafke jabun kudi har N17m ana tsaka da karancin naira, mutane 3 sun shiga uku


Rundunar yan sandan jihar Kebbi ta sanar da kama wasu mutane bisa zargin mallakan jabun kudi na Naira miliyan 17 a jihar. Shafin labarai na yanar gizo isyaku.com ya samo.

Dubun mutanen ua cika ne a garin Warrah da ke karamar hukumar Ngaski a jihar Kebbi.

Kwamishinan Yan sandan jihar Kebbi Ahmed Magaji Kontagora ya sanar wa manema labarai a garin Birnin kebbi ranar 20 ga watan Fabrairu.

Ya ce:

" Jami’an ‘yan sanda da ke ofishin ‘yan sanda na Warrah tare da taimakon kungiyar ma’aikatan sufuri ta kasa (NURTW) a tashar mota ta Warrah ranar  29/01/2023. 

Sun kama wasu mutane 3 dauke da takardun kudi na kudi naira miliyan goma sha bakwai.  (N17,000,000), wanda ake zargin jabun ne. 

Wadanda ake zargin su ne: Faruku Zubairu (2) Ibrahim Musa da (3) Salisu Mohammed duk na kauyukan Gungun Tawaye da Chupamini, a karamar hukumar Ngaski.  

An kammala bincike kuma nan ba da dadewa ba za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban Kotu". 

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN