Soji sun bindige barawon akwatin zabe a jihar Kogi


Jami'an soji sun bindige wani da ake zargin ya sace akwatin zabe a hanyar Ogege, Mazabar Odaba a gundumar Dekina jihar Kogi.

 Intelregion ta rahoto an tattaro cewa masu kada kuri’a a yankin sun tsere daga filin kada kuri’a sakamakon ayyukan ‘yan bangar siyasa da suka zo da yawa domin lalata kayayyakin zabe.

 ‘Yan barandan da suka bayyana dauke da adduna da bindigu sun yi awon gaba da akwatunan zabe tare da karya kujeru tare da tarwatsa masu kada kuri’a.

Bayan harin, an soke zaben mazabu bakwai na mazabar Kogi ta Gabas, inda aka soke rumfunan zabe biyu a Anyigba da ke yankin karamar hukumar Dekina, da sauran biyar a karamar hukumar Omala ta jihar Kogi.

 A wani labarin kuma, an ce an kashe mutane biyu a unguwar Ndi Agwu da ke Abam a karamar hukumar Arochukwu a jihar Abia.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN