Wasu gungun mutane a jihar Legas sun shirya wata zanga-zanga a hedkwatan bankunan kasuwanci da yawa a birnin Legas. Legit.ng ya ruwaito.
A wani bidiyon da aka yada a kafar sada zumunta, ‘yan zanga-zangan sun zargi bankuna da kin bin ka’idar CBN game da sabbin kudi, lamarin da ya ke ba talakawan kasar wahala.
An shirya wannan zanga-zanga ne karkashin kungiyar farar hula ta Coalition of Civil Society Organizations for Good Governance, (CCSGG).
A lokacin zanga-zangar, kungiyar ta yi kira ga bankuna da su saki sabbin Naira ga kowa a Najeriya don ci gaba da harka yadda aka saba.