Daga karshe: Hukumar yan sanda ta yi magana kan mutumin da ya mutu a banki cikin layi

 


Delta - Wani kwastoman banki ya yanke jiki ya fadi matacce cikin harabar wani banki bayan kwashe awanni kan layi a garin Agbor na jihar Delta. Legit.ng yawallafa.


Wannan abu ya auku ne ranar Alhamis, 2 ga watan Febrairu, 2023 a karamar hukumar Ika ta kudu, rahoton Tribune.


Kakakin hukumar yan sandan jihar Delta, DSP Bright Edafe, ya tabbatar da aukuwan wannan lamari.


DSP Bright Edafe ya ce mutumin ya shiga bankin karban katin ATM dinsa ne.


A cewarsa:


"Labarin dake yawo cewa wani mutumi ya yanke jiki ya fadi matacce yayin kokarin cire kudi ba an yi karin gishiri cikin miya. Ya yanke jiki ya fadi ne yayin layin karban sabon katin ATM."

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN