Da duminsa: Babura da aka gani cike a mota a Masarautar Zuru na Yan bindigan ne? Duba gaskiyar abin da ya faru

 

Illustrative picture

Rahotanni na cewa babu wani dan bindiga da jami'an tsaro suka kashe a yankin jihar Kebbi cikin yan kwanakin nan.


Wasu rahotannin daga majiyoyi da dama na cewa jami'an tsaro sun yi artabu ne da yan bindiga a yankin Zamfara ba a yankin jihar Kebbi ba yan kwanakin da suka gabata.


Wannan na zuwa ne bayan jita-jita ya kaure a Masarautar Zuru cewa an kashe dukkan yan ta'addan da ke addabar yankin Kanya da sassan karamar hukumar Danko Wasagu.


Rahotun na cewa an ga mota makare da babura da sauran kayaki wadanda ake zargin na yan bindigan ne.


Lamari da ya sa wasu Yan siyasa suka fara yada jita jita domin alakanta lamarin da nasara da suka gaza samu a Masarautar Zuru tun 2015.


Yanzu dai ta tabbata cewa karya ne zancen kashe yan bindigan a Masarautar Zuru da kewaye. 


Gwamnatin jihar Kebbi na kashe miliyoyin kudin jama'ar jihar Kebbi da sunan tafiyar da harkar tsaro a Masarautar Zuru. Sai dai tun 2015, har zuwa wannan lokaci ta kasa samar da tsaron da take ikirarin fitar da miliyoyin naira domin tafiyarwa a Masarautar Zuru. 

4 Comments

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

  1. Indai gaskiyane miyasa bazaa nunamana gawakinsuba saina babura jamaa karfa amaidamu kaman jahulai.
    Kuma wlh kuji tsoron allah

    ReplyDelete
  2. Allah ya kawo muna dauki

    ReplyDelete
  3. Gwamnati tasan inda tanya,adds duke saboda haka munbarsu ga Allah

    ReplyDelete
  4. Allah yayi muna mafita, ya saka tausayi a zukatan shuwagabannin mu, badon halin mu ba😭🙏

    ReplyDelete
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN