Canjin kudu: Ku tsige "shi" ku kori Gwamnan CBN daga ofis, ku gurfanar da shi a Kotu, fusataccen Malamin addini ya magantu



Wani malamin addinin Bishop Abraham Chris Udeh, ya bayyana rashin jin dadinsa a kan sanarwar da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi a ranar Alhamis, na cewa tsohon takardun kudi na Naira 1,000 da N500 su daina aiki daga jiya. Jaridar vanguard ta ruwaito.

 Don haka ya bukaci majalisar dokokin kasar da ta yi amfani da ikon da sassan da suka dace na kundin tsarin mulkin Najeriya suka ba su na tsige shugaba Buhari saboda yunwa da wahala da aka jefa ‘yan Najeriya da sunan tsara tattalin arziki ta hanyar yin musanya da sabbin takardun kudi na Naira.

 Bishop Udeh wanda kuma shi ne babban mai kula da Mount Zion Faith Global Liberation Ministries (aka "By Fire By Fire"), Nnewi, jihar Anambra, ya ce ya kamata a kori Gwamnan Babban Bankin CBN, Godwin Emefiele daga ofis sannan kuma a gurfanar da shi gaban kotu.  domin cin mutuncin yan Najeriya.

 Ya ce abin takaici ne yadda ’yan Najeriya ke yawo a kan tituna suna neman sabbin takardun Naira ba tare da samun biyan bukata ba, kuma su Buhari da Emefiele sun shagaltu da gaya musu cewa su yi hakuri su jira su sabbin takardun Naira a lokacin da talakawa ke mutuwa saboda yunwa.

 Ya ce abin da ya fi daure kai shi ne yadda gwamnatin tarayya ta ki bin umurnin kotun koli na ba da damar tsohon takardun naira su zauna tare da sabbin takardun har zuwa ranar 22 ga watan Fabrairu a lokacin da ake sa ran kotun koli za ta yanke hukunci na karshe kan karar da wasu Gwamnonin jihohi suka shigar suna adawa da gwamnatin tarayya dangane da batun sabon kudin Naira.

BY ISYAKU.COM

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN