Wata mata ta mutu a dakin otal, makwabta sun gudu


An gano gawar wata mata mai zaman kanta a dakin Otal a kan hanyar tsohuwar kasuwa a birnin Onitsha na jihar Anambra. Shafin labarai n isyaku.com ya ruwaito.

Majiyarmu ta ce matar yar asalin jihar Enugu ce kuma sunanta Chisom, ta mutu ne ranar Litinin 30 ga watan Janairu 2023 bayan ta gama wanke kwanonin abinci. 

An tarar da gawarta rataye a dakin Otal. Sai dai har yanzu ba a san musabbabin mutuwarta ba.

Chisom tana zaune a dakin otal. Sai dai makwabta sun gudu bayan sun sami labarin mutuwarta.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN