Siyasar Zamfara: Kotu ta soke hukuncin hana PDP takarar Gwamnan jihar Zamfara


Kotun Daukaka Kara ta soke Hukuncin Babbar Kotun Tarayya da ta haramta wa Jam’iyyar PDP shiga zaben Gwamnan Jihar Zamfara a 2023. Jaridar Aminiya ta ruwaito.

Kotun Daukakarar da ke zamanta a Sakkwato ta tabbatar Dauda Lawal Dare a matsayin halastaccen dan takarar PDP a zaben da ke tafe a watan Maris.

Hakan kuwa na zuwa ne bayan da farko Babbar Kotun Tarayya da ke Gusau, babban birnin Jihar Zamfara ta soke zaben da Dauda Lawal ya lashe a matsayin dan takarar gwamnan PDP na Jihar Zamfara.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN