Fada ya barke a Senegal bayan da dan majalisa ya mari wata abokiyar aikinsa saboda ta zagi shugabar addini yayin zaman majalisar kai tsaye (bidiyo)


Hatsaniya ta barke a majalisar dokokin kasar Senegal a ranar alhamis 1 ga watan Disamba bayan da wani dan majalisar adawa namiji ya mari wata abokiyar aikinsa mace a fuska, a daidai lokacin da ake samun rashin jituwa tsakanin ‘yan jam’iyya mai mulki da ‘yan adawa. Shafin labarai na isyaku.com ya samo.

Takaddama ta kaure tsakanin 'yan siyasa masu mulki da na adawa tun bayan zaben 'yan majalisar dokokin kasar da aka gudanar a watan Yuli inda jam'iyyar mai mulki ta rasa rinjayen da take da shi, saboda damuwar da shugaba Macky Sall ya yi na neman wa'adi na uku a shekara ta 2024.

'Yar majalisar dokokin kasar Massata Samb a ranar Alhamis din da ta gabata ta yi jawabi ga majalisar game da kalaman Amy Ndiaye Gniby ta jam'iyyar gamayyar jam'iyyar Benno Bokk Yakaar (BBY) mai mulki, ta yi a karshen mako inda ta soki wani shugaba mai adawa da wa'adi na uku na Sall.

A yayin da ake ci gaba da gabatar da kasafin kudin, dan majalisar dokokin kasar Massata Samb, dan adawar ya zarce inda ya cakaki Amy Ndiaye Gniby ta jam'iyyar hadaka ta Benno Bokk Yakaar (BBY) mai mulki, lamarin da ya haifar da ce-ce-ku-ce.

A ramuwar gayya Gniby ta jefi Samb da kujera kafin wani dan majalisa ya kai ta falon.  An dai dakatar da zaman ne yayin da ‘yan majalisar suka rika cin zarafi da zagi da cin mutunci tsakaninsu.

 Kalli bidiyo a kasa


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN