Zaben 2023: Jihohi 5 masu karfi na APC da watakila Tinubu bazai ci zabe ba da kuma dalili


Ko da yake ana sa ran cewa ‘yan takarar shugaban kasa a zabukan Najeriya sun lashe jihohin da gwamnonin ke cikin jam’iyyunsu, akwai yiwuwar a samu wasu ketare a 2023. Legit.ng ta ruwaito.

Saboda akalla abubuwa biyu, mai yiwuwa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC), Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya kasa yin nasara a wasu jihohin da gwamnonin ke zaune a jam’iyya mai mulki.

Jihohin sun hada da:

Jihohin Cross River Ebonyi Imo Kwara da Ogun.

Idan har ba a magance rikicin gabanin kada kuri’a ba, tsohon shugaban majalisar dattawa, Bukola Saraki na iya yin amfani da wannan damar wajen ganin PDP ta yi wa Tinubu illa a yankin arewa ta tsakiya.

Jihohin Imo da Ebonyi

Shiyyar kudu maso gabas ba masoyan jam'iyyar APC mai mulki bane.  Tun a shekarar 1999, yankin da 'yan kabilar Igbo ke da rinjaye suka zabi jam'iyyar PDP.

A 2023, yanzu suna da zabi biyu: PDP ko Labour Party, wanda ke tsayar da dan su Peter Obi a matsayin dan takarar shugaban kasa.

Don haka, duk da cewa gwamnonin Imo da Ebonyi na APC, da wuya Tinubu ya kayar da Atiku ko Peter Obi a jihohin Kudu maso Gabas biyu a zaben 2023.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN