Manoma biyu sun mutu bayan motarsu ta bi ta kan nakiya da yan Ta'adda suka binne a Kaduna


Wasu mutane sun mutu a yayin da wata mota da suke ciki taka nakiya da ‘yan ta’adda suka binne a Kaduna

Wasu ‘yan kasa biyu sun mutu a wani harin nakiya da aka binne a karamar hukumar Chikun ta jihar Kaduna.

Kwamishinan tsaro na cikin gida da harkokin cikin gida na jihar, Samuel Aruwan, ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ya fitar a yammacin ranar Alhamis, 3 ga watan Nuwamba, 2022.

Sanarwar ta kara da cewa, "Lamarin ya faru ne da misalin karfe 2:00 na yammacin ranar Alhamis lokacin da motar wadanda abin ya shafa ta bi ta kan wata nakiya da 'yan ta'adda suka binne a wani wuri da ake kira Zangon Tofa, a yankin Kabrasha."

'Yan kasar na jigilar amfanin gona da aka girbe lokacin da lamarin ya afku.

Kwamishinan ya kara da cewa, “Mutane biyun da suka rasa rayukansu sunayensu Babajo Alhaji Tanimu da Safiyanu Ibrahim, gwamnati na jiran karin bayani.

A halin da ake ciki, Gwamna Nasir El-Rufai ya jajanta wa iyalan ‘yan kasar bisa wannan mummunan lamari.

Gwamnan wanda ya yi addu’ar Allah ya jikan wadanda lamarin ya shafa, ya kuma yi kira ga mazauna yankin da su kwantar da hankalinsu.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN