Kotu ta sake soke zaben fidda gwani na Gwamnan Jihar Zamfara na PDP ta ce PDP ba za ta tsayar da kowane dan takara ba a zaben Gwamna 2023 a jjhar

Kotu ta sake soke zaben fidda gwani na Gwamnan Jihar Zamfara na PDP ta ce PDP ba za ta tsayar da kowane dan takara ba a zaben Gwamna 2023 a jjhar


Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Gusau, babban birnin jihar Zamfara, ta sake soke zaben fidda gwani na takarar gwamna na jam'iyyar PDP wanda ya fito da Dauda Lawal-Dare a matsayin dan takararta a ranar Talata 8 ga watan Nuwamba.

Mai shari’a Aminu Bappa ya kuma ce jam’iyyar PDP ba za ta tsayar da kowane dan takara a zaben Gwamnan jihar a 2023 ba.

Wannan na zuwa ne watanni biyu bayan da wata kotu ta soke zaben fidda gwanin da ya gabata wanda ya zabi Lawal-Dare sakamakon karar da Ibrahim Shehu da wasu ‘yan takara biyu suka shigar na kalubalantar sahihancin zaben fidda gwani.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN