Dan Majalisar da ya yanke jiki a taron kaddamar da yakin neman zaben Tinubu ya rasu


Dan Majalisar Dokokin Jihar Legas mai wakiltar mazabar Mushin II, Sobur Olayiwola Olawale ya rasu. Jaridar Aminiya a ruwaito.

Olawale wanda aka fi sani da Omititi, na cikin ‘yan siyasar da suka halarci taron kaddamar da yakin neman zaben dan takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Tinubu a Jos, babban birnin Jihar Filato.

Rahotanni sun bayyana cewa marigayin ya yanke jiki ya fadi a wajen taron kuma daga bisani ya ce ga garinku nan.

Wani jigo a jam’iyyar APC da ya nemi a sakaya sunansa ya shaida wa Aminiya cewa ko a karshen makon da ya gabata suna tare da Olawale.

“Mun hadu ne a gidan Sanata Ganiyu Olanrewaju Solomon (GOS) a ranar Lahadi, inda muka gaisa. Kuma a wancan lokacin yana cikin koshin lafiya.

“Koma mene ne amma da alamu mutuwarsa na da alaka da hawan jini. Amma mutuwarsa ta girgiza mu.”

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN