An kashe shugaban mata na jam'iyyar Labour a Kaduna


Wasu ‘yan bindiga da ake kyautata zaton makasa ne sun kashe Mrs Victoria Chintex, shugabar mata ta jam’iyyar Labour a karamar hukumar Kaura ta jihar Kaduna
.

Rahotanni sun ce ‘yan bindigar sun kai farmaki gidanta ne a daren ranar Litinin 28 ga watan Nuwamba, 2022, inda suka harbe ta har lahira yayin da mijinta ya samu rauni a kafarsa.

Edward Simon Buju, Sakataren Yada Labarai na Jam’iyyar Kwadago ta Shiyya ta 3 a Jihar Kaduna, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa a ranar Talata, ya bayyana marigayiyar shugabar mata a matsayin mace mai kwazo da ta mutu a daidai lokacin da jam’iyyar da kuma kasa baki daya ta fi bukata.

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN