Wasu ‘yan bindiga da ake kyautata zaton makasa ne sun kashe Mrs Victoria Chintex, shugabar mata ta jam’iyyar Labour a karamar hukumar Kaura ta jihar Kaduna.
Rahotanni sun ce ‘yan bindigar sun kai farmaki gidanta ne a daren ranar Litinin 28 ga watan Nuwamba, 2022, inda suka harbe ta har lahira yayin da mijinta ya samu rauni a kafarsa.
Edward Simon Buju, Sakataren Yada Labarai na Jam’iyyar Kwadago ta Shiyya ta 3 a Jihar Kaduna, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa a ranar Talata, ya bayyana marigayiyar shugabar mata a matsayin mace mai kwazo da ta mutu a daidai lokacin da jam’iyyar da kuma kasa baki daya ta fi bukata.