Boka ya bindige kwastoma har Lahira yayin da yake gwajin layar kare harsashi a jikinsa


Rundunar ‘yan sandan jihar Enugu ta kama wani boka dan shekara 23 mai suna Odoh Emmanuel, wanda ya bindige wanda yake kwastoma a lokacin da yake gwada ingancin maganin bindiga da ya tanadar wa marigayin. Shafin isyaku.com ya samo.

Kakakin rundunar Yan sandan jihar, DSP Daniel Ndukwe, wanda ya bayyana hakan a wata sanarwa a ranar Talata, 29 ga watan Nuwamba, 2022, ya ce lamarin ya faru ne a karamar hukumar Isi-Uzo da ke jihar.

A cewar PPRO, wanda ake zargin ya harbi marigayin, Onunze Benedict, da wata bindigar da aka kera ta gida a cikin wurin ibadar sa a lokacin da yake gwada karfin maganin bindigar.

“A ranar 16/11/2022 da misalin karfe 11:00 na rana, jami’an ‘yan sanda da ke aiki a sashin ‘yan sanda na Isi-Uzo na rundunar ‘yan sanda sun kama Odoh Emmanuel (Namiji kuma boka dan asalin jihar) mai shekaru 23 a kauyen Umuaram da ke unguwar Ikem a karamar hukumar Isi-Uzo.  Sanarwar ta kara da cewa, saboda harbi da kuma kashe wani baligi mai suna Onuze Benedict, dan kabilar Eha-Amufu a karamar hukumar. 

“Bincike na farko ya nuna cewa wanda ake zargin ya amsa laifin yin amfani da bindiga da aka kera a cikin gida wajen harbi da kuma kashe kwastoma a wurin ibadarsa a wurin da aka ambata, a lokacin da yake gwada bajintar kariya daga harbin bindiga da ya shirya masa.

"An gano bindigar, yayin da ake ci gaba da bincike a sashin kisan kai na CID na jihar Enugu."

 Za a gurfanar da wanda ake zargin da zarar an kammala bincike.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN