Yadda mai gidan haya ta damfari masu neman gida su 200 ta karbe kudinsu a kan gida daya

Yadda mai gidan haya ta damfari masu neman gida su 200 ta karbe kudinsu a kan gida daya


Wani abin ban mamaki ya faru a lamba 22, Titin Anuoluwapo, a unguwar Ejigbo a jihar Legas, bayan kimanin masu neman gidaje 200 da suka biya makudan kudade don masauki sun gano cewa matar mai gida wani bene mai hawa daya ta yaudare su. Kudirat.

Punch ta ruwaito cewa Kudirat ta hada baki da wani wakili mai suna Tunde Nojeemdeen domin aikata wannan zamba, ta hanyar tura su wajensa lokacin da suka tambayi haya a ginin.

Sai dai da zuwa gidan a ranar Asabar, 24 ga watan Satumba, masu neman gidan sun gano cewa adadin masu haya ya zarce gidaje 14 da ake da su.

Oluwakemi Sodiq, daya daga cikin wadanda abin ya shafa ya shaida wa manema labarai cewa an kai rahoton lamarin a ofishin ‘yan sanda na Ejigbo, daga bisani kuma aka mika shi zuwa sashin binciken manyan laifuka na jihar, Yaba. Ta kuma bayyana cewa masu neman hayar sun biya kudade daga N300,000 zuwa N500,000.

Yawancin wadanda abin ya shafa kuma sun yi ikirarin cewa an jefar da su daga gidajensu na da.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Legas, Benjamin Hundeyin wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce an kama Nojeemdeem.

Hundeyin ya ce; 

 "Yanzu haka yana tsare."

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN