Type Here to Get Search Results !

Miji ya rusa gidajen da ya gina wa matarsa ​​da mahaifiyarta bayan ta yi watsi da shi saboda wani mutum, duba yadda ta faru

Wani mutum ya rusa gidajen da ya gina wa matarsa ​​da mahaifiyarta bayan ta yi watsi da shi saboda wani mutum, duba yadda ta faru


Wani dan kasar Malawi mai suna Francis Banda ya rusa gidajen da ya gina wa matarsa ​​da mahaifiyarta bayan matar ta rabu da shi saboda wani mutum. Shafin labarai na yanar gizo isyaku.com ya samo.

A wani faifan sauti da aka watsa a shafukan sada zumunta, Banda ya ce shi da matarsa ​​sun yi aure shekara 13 kuma suna da ‘ya’ya uku, kamar yadda Malawi 24 ta ruwaito.

Ya kara da cewa a lokacin aurensu ya yi nasarar gina gidaje biyu daya na matar daya kuma na mahaifiyarta a kauyen uwargidan.

A cewar Banda, matarsa ​​ta fara dangantaka da wani mutum, kuma kwanan nan ta bar gidansu ta koma wajen mutumin. 

A wani lokaci Banda ya yi ƙoƙarin yin magana da matan a wayar salula, amma sai sabon mutumin ya amsa kiran wayarta .

Hakan ya fusata Banda ya yanke shawarar rusa gidajen da ya gina wa matar da mahaifiyarta a kauyensu. 

Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Hollywood Movies