Rikicin Hausawa da ƙabilu a Sudan ya kashe mutum 200


Jami'ai a Sudan sun ce yawan mutanen da suka mutu a rikicin ƙabilanci da ake yi a kudancin kasar tsakanin Hausawa da 'yan kabilar Berta ya ƙaru zuwa 200.

BBC ta ruwaito wani shugaban al'umma a Jihar Blue Nile ya ce an yi kashe-kashen ne a kauyuwa uku, inda ya yi kira ga kungiyoyin agaji da su taimaka wajen binne gawarwakin wadanda suka rasu.

Rahotanni na cewa ana rikici tsakanin Hausawa da Berta ya ɓarke ne kan gonaki.

A jiya Juma'a aka sanya dokar ta-ɓaci ta tsawon kwana 30 a fadin jihar ta Blue Nile.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN