PDP reshen jihar Kebbi ta musanta yin babban nadi gabanin ziyarar dan takararta na shugaban kasa - ISYAKU.COM


Jam’iyyar PDP reshen jihar Kebbi ta musanta nada Janar Ishaya Bamaiyi mai ritaya a matsayin daraktan yakin neman zaben shugaban kasa a jihar.

Shugaban jam’iyyar PDP na jihar, Alhaji Usman Suru ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a ranar Laraba a Birnin Kebbi, yayin da yake mayar da martani ga wani rahoto da aka samu ta yanar gizo.

 “An jawo hankalin jam’iyyar PDP a jihar Kebbi a wata hira da manema labarai da Alhaji Kabiru Tanimu Turaki ya yi wa manema labarai, kuma jaridar Blueprint Newspaper ta wallafa a takenta na yanar gizo: PDP ta nada Janar din yakin neman zaben Atiku na shugaban kasa a Kebbi.

“Tattaunawar da aka yi a kafafen yada labarai da ake magana a kai da jama’a musamman ‘yan jam’iyyar PDP na jihar Kebbi aka nada Janar Ishaya Bamaiyi a matsayin Darakta Janar na yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar PDP a jihar Kebbi.

“Muna so mu bayyana dalla-dalla cewa nadin shine tunanin Kabiru Tanimu Tukari.

“Hakika an kafa tsarin yakin neman zaben shugaban kasa a jihar Kebbi kamar yadda shugabannin jam’iyyar na kasa suka ba da umurni wata daya da ya gabata, Majalisar Kamfen din na karkashin jagorancin Dakta Bello Haliru,” inji shi.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN