Da dumi-dumi: Yan bindiga sun dira tsakanin garuruwan Marafa da Mahuta sun tafka satar shanu a Masarautar Zuru

Da dumi-dumi: Yan bindiga sun dira tsakanin garuruwan Marafa da Mahuta sun tafka satar shanu a Masarautar Zuru


Rahotanni daga Masarautar Zuru a kudancin jihar Kebbi na cewa Yan bindiga sun shiga yankin Marafa zuwa Mahuta suka saci shanaye da ba a san adadinsu ba kawo yanzu.

Rahotannin sun kara da cewa kawo yanzu ba a sami labarin asarar rayuka ba a harin na ranar Alhamis. Sai dai majiyarmu ta shaida mana cewa jama'a sun yi asara dabbinsu ga yan bindigar wanda suka shiga yankin da sanyin safiyar Alhamis.

Wata majiya da bata son a ambaci sunanta ta shaida mana cewa an gan jami'an soji da yan banga sun shiga yankin domin fuskantar lamarin.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN