Allah ya yi wa Ibrahim Musa Argungu tsohon SA Media na tsohon Gwamnan jihar Kebbi Saidu Dakingari rasuwa


Allah ya yi wa Ibrahim Musa Argungu rasuwa ranar Lahadi 2 ga watan Oktoba 2022.

Kafin rasuwarsa ya taba aiki da Kamfanin karafa na Ajaokuta, daga bisani ya yi aiki da Gwamnatin jihar Kebbi a matsayin S.A Media ga Gwamnan jihar Kebbi na waccan lokaci Saidu Nasamu Dakingari.

Ibrahim kane ne ga Muhammad Musa Argungu Tambarin Kabi

Ya rasu ya bar mata biyu da yara biyu.

An yi Jana'izarsa ranar Litinin 4 ga watan Oktoba da karfe 10 na safe a Kaduna.

Allah ya jikansa ya gafarta masa.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN