Mutane 6 sun makale yayin da wani gini mai hawa 7 ya rufta a Lekki da ke jihar Legas.


Mutane 6 sun makale yayin da wani gini mai hawa bakwai ya rufta a Lekki da ke jihar Legas.

Mista Ibrahim Farinloye, Ko’odinetan shiyyar Kudu maso Yamma, Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Kasa (NEMA), ya tabbatar wa Kamfanin Dillancin Labarai na NAN, afkuwar lamarin a ranar Lahadi a Legas.

Farinloye ya ce ginin da ke kan titin Oba Idowu Oniru, Lekki, ana kan gina shi ne a lokacin da ya ruguje.

Ya ce da alama mutane shida sun makale a karkashin baraguzan ginin.

Wadanda suka kai daukin gaggawa sun hada da rundunar ‘yan sandan Najeriya, NEMA da kuma hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Legas (LASEMA).

Ana ci gaba da gudanar da ayyukan agaji kawo lokacin rubuta wannan rahoton. 

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN