Yanzu yanzu: Jami’in hukumar FRSC ya caka wa direba wuka har lahira



Wani jami’in hukumar kiyaye haddura ta kasa FRSC da har yanzu ba a tantance ko waye ba ya kashe wani direban motar safa da wuka har lahira a karamar hukumar Isiala Ngwa a jihar Abia. Shafin Isyaku News isyaku.com ya samo.

An tattaro cewa lamarin ya faru ne a mahadar Umuikaa, daura da hanyar Fatakwal - Aba - Enugu Expressway a ranar Talata, 16 ga watan Agusta. 

Wasu shaidun gani da ido sun shaidawa Vanguard cewa an samu rashin jituwa tsakanin jami’an hukumar ta FRSC biyu da direban motar, wanda ya kai ga fada. A cikin rudanin da aka samu, daya daga cikin jami’an hukumar FRSC ya caka wa direban wuka a bayansa.

Jami’an FRSC sun kai direban asibitin Ronald da ke Mkpuka, inda Likitoci suka tabbatar da mutuwarsa. 

Anyatonwu a wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Enyinnaya Standhope Nwaigwe ya fitar, ya bukaci kwamandan hukumar FRSC na jihar da ya gaggauta binciki lamarin tare da damke wadanda suka aikata laifin.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN