Yanzu-yanzu: Gwamna Bagudu ya amince da nadin Hakimai 12 a jihar Kebbi


Gwamna Abubakar Bagudu na jihar Kebbi, ya amince da nadin Hakimai 12 a kananan hukumomi tara na jihar. Shafin Isyaku News isyaku.com ya samo.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da babban sakataren ma’aikatar kananan hukumomi da Masarautu, Muhammed Sani-Umar ya fitar ranar Talata a Birnin Kebbi.

Sani-Umar ya nakalto Gwamnan yana taya hakiman gundumomi murna tare da yi musu fatan Allah ya yi musu jagora da kuma kariya a kan sabon aikin da aka dora musu. Kampanin dillancin labarai na Najeriya NAN ta ruwaito. 

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN