Yan Bindiga: Tsohon Sarki da aka tsige daga mukaminsa a Zamfara ya rasu a Dubai


Tsohon Sarkin Zurmi na jihar Zamfara Abubakar Atiku ya rasu a birnin Dubai na kasar Hadaddiyar Daular Larabawa. Shafin labarai na isyaku.com ya samo.

Atiku ya rasu ne a wani asibiti mai zaman kansa bayan ya sha fama da rashin lafiya. 

Ku tuna cewa an tsige marigayin ne  tare da Sarkin Dansadau, Husaini Umar a ranar 27 ga Afrilu, 2021, bisa zargin taimakawa ‘yan fashi a masarautun su  .

Wani dan uwa mai suna Sani Zurmi, wanda ya tabbatar wa jaridar Punch cewa har yanzu ba a kawo gawar zuwa Najeriya domin binnewa ba.

“Har yanzu gawarsa tana Dubai saboda rashin samun jirgin da zai dawo da marigayin gida domin yi masa jana’iza,” in ji Zurmi.

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN