Yan Bindiga: Tsohon Sarki da aka tsige daga mukaminsa a Zamfara ya rasu a Dubai


Tsohon Sarkin Zurmi na jihar Zamfara Abubakar Atiku ya rasu a birnin Dubai na kasar Hadaddiyar Daular Larabawa. Shafin labarai na isyaku.com ya samo.

Atiku ya rasu ne a wani asibiti mai zaman kansa bayan ya sha fama da rashin lafiya. 

Ku tuna cewa an tsige marigayin ne  tare da Sarkin Dansadau, Husaini Umar a ranar 27 ga Afrilu, 2021, bisa zargin taimakawa ‘yan fashi a masarautun su  .

Wani dan uwa mai suna Sani Zurmi, wanda ya tabbatar wa jaridar Punch cewa har yanzu ba a kawo gawar zuwa Najeriya domin binnewa ba.

“Har yanzu gawarsa tana Dubai saboda rashin samun jirgin da zai dawo da marigayin gida domin yi masa jana’iza,” in ji Zurmi.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN