Wasu samari 2 sun yi garkuwa da 'dan makwabcinsu mai shekara 13 suka shake shi har Lahira a jihar Niger, duba dalili


Jami’an rundunar ‘yan sandan jihar Neja sun cafke wasu mutane biyu da ake zargin sun yi garkuwa da dan makwabcinsu dan shekara 13 a karamar hukumar Tafa da ke jihar. Kafar labarai na yanar gizo Isyaku News Online (isyaku.com) ya samo.

Kakakin rundunar, DSP Wasiu Abiodun, a wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin, 1 ga watan Agusta, ya ce an kama wadanda ake zargin Usman Sabiu da Nafiu Umar ne biyo bayan rahoton da rundunar ta samu a ranar Asabar, 30 ga watan Yuli kan yaron da ya bata mai suna Yasir Salisu.

A cewar PPRO, wadanda ake zargin sun sace yaron ne da nufin karbar Naira 100,000 daga hannun mahaifinsa. 

Da aka yi masa tambayoyi, Sabiu ya amsa cewa sun shake yaron har lahira kuma sun binne shi a wani kabari mara zurfi saboda bai iya samar da lambar wayar salula na mahaifinsa da za su yi amfani da shi domin neman kudin fansa ba kuma ya gane su. 

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN