Labari mai dadi: Hukumar kula da shige da fice ta Najeriya NIS na shirin daukar karin ma'aikata 5000


Mukaddashin Kwanturola-Janar na Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS), Mista Idris Jere, ya ce ana shirin daukar karin ma’aikata 5,000 a ma’aikatar. Shafin isyaku.com ya samo.

Kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN ta ruwaito cewa Jere, wanda ya bayyana hakan a lokacin da yake amsa da tambayoyi daga manema labarai a Dutse ranar Asabar, ya ce an dauki matakin ne da nufin magance matsalar karancin ma’aikata a hukumar NIS.

“Game da rashin isassun ma’aikata a NIS, kamar yadda kuka sani, yanzu mun kammala daukar ma’aikata kuma muna horar da wadanda aka dauka a yanzu.

“Kamar yadda kuka sani, gwamnati ta sanya takunkumin daukar ma’aikata, amma ta dage hakan a kan jami’an tsaro, domin tsaro shi ne muhimmin abu.

"Don haka, mun rubuta wa shugaban kasa kuma ina da tabbacin za mu samu amincewar daukar karin ma'aikata kusan 5,000 a cikin NIS," in ji Jere.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN