Gwamna Bagudu ya sake tafka wani abin alheri ga matasa yan jihar Kebbi da suka shiga aikin soji, yan sanda da sauransu


Gwamnan jihar Kebbi, Sanata Abubakar Atiku Bagudu, ya amince da sakin naira miliyan goma sha bakwai da dubu dari hudu a matsayin tallafin kudi ga matasa yan jihar Kebbi masu zuwa horo kan aikin soja da na kaki gaba daya. Shafin Isyaku News Online isyaku.com ya samo.

Amincewar na kunshe ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun mukaddashin shugaban ma’aikata na jihar Kebbi, Alhaji Safiyanu Garba Bena kuma aka rabawa manema labarai a Birnin Kebbi a ranar Litinin din nan.

A cewar sanarwar, jimillar matasa 369 ‘yan asalin jihar Kebbi ne za su je domin samun horon ‘yan sandan Najeriya a matsayin ‘yan sanda, ‘Direct Short Service da Direct  Combatant Commission of the Nigerian Army, da kuma gudanar da aikin daukar ma’aikata a shekarar 2022. Da Kuma wadanda suka shiga Rundunar Sojan Sama ta Najeriya a matsayin Airmen /AirWomen.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, matakin da Gwamna Bagudu ya yi na da nufin rage zaman kashe wando a tsakanin matasa masu tada zaune tsaye a jihar, da kuma kudurin wannan gwamnati na cike kason jihar yadda ya kamata a yankunan da aka ambata

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN