2023: Bayan rashin halartar taron NBA, Tinubu ya samu damar yin magana tare da Atiku, Obi a wani taron


Kasa da sa'o'i 24 da bude taron kungiyar lauyoyin Najeriya, an gayyaci 'yan takarar uku na Atiku Abubakar, Peter Obi, da Bola Tinubu zuwa gasa ta Unity Polo, a jihar Keffi-Nasarawa.

PM News ya ruwaito cewa taron zai shaida kasancewar sauran jiga-jigan siyasa, sarakuna, da sauran masu ruwa da tsaki a kasar.

An bayyana hakan ne a ranar Talata, 23 ga watan Agusta a Abuja ta hannun wanda ya kafa kuma mai tallata taron, Mista Ahmed Wadada.

Kamar yadda sanarwar da mai shirya taron ya fitar, taron zai bude wani dandali na fahimtar juna a tsakanin ‘yan takarar shugaban kasa da za su fafata a babban zaben 2023 mai zuwa.

Yace:

“Tuni yanayin siyasar kasar ya fara daukar nauyi kafin fara yakin neman zaben dukkan ‘yan takarar shugaban kasa.

"Zai iya zafi a cikin watanni biyu masu zuwa, don haka bukatar gasar don kawar da tashin hankali a fagen siyasa.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN