Sanata Ademola Adeleke na jam’iyyar PDP ya doke Gwamna Gboyega Oyetola na jam’iyyar All Progressives Congress a gidan gwamnatin Osun. Kafar labarai na yanar gizo isyaku.com ya samo.
Adeleke ya samu kuri’u 117 a mazabar Agowande/Oshogbo GRA/ Mazabar gidan Gwamnati, yayin da Oyetola ya samu kuri’u 106.
Mazabar na karamar hukumar Olorunda. Ana ci gaba da kidayar kuri'un da aka kada a zaben Gwamnan jihar da aka gudanar a yau 16 ga watan Yuli.