Zaben Osun: Adeleke na PDP ya doke Gwamna Oyetola na APC a Mazabar gidan gwamnatin Osun


Sanata Ademola Adeleke na jam’iyyar PDP ya doke Gwamna Gboyega Oyetola na jam’iyyar All Progressives Congress a gidan gwamnatin Osun. Kafar labarai na yanar gizo isyaku.com ya samo.

Adeleke ya samu kuri’u 117 a mazabar Agowande/Oshogbo GRA/ Mazabar gidan Gwamnati, yayin da Oyetola ya samu kuri’u 106.

Mazabar na karamar hukumar Olorunda. Ana ci gaba da kidayar kuri'un da aka kada a zaben Gwamnan jihar da aka gudanar a yau 16 ga watan Yuli. 

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN