Rikicin PDP: Atiku na shirin dawowa daga kasar waje domin daukar muhimmin mataki biyo bayan rade radin yiwuwar ficewar Wike daga jam'iyar


Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, na shirin dawowa daga tafiyar da ya yi zuwa kasashen waje domin ganin bayan rikicin da ke ci gaba da rikita jam’iyyar kan zaben wanda zai yi takara
.

Wani rahoto da Daily trust ta samu ya nuna cewa manyan jiga-jigan jam’iyyar ba su ji dadin ziyarar da gwamnonin jam’iyyar All Progressives Congress (APC) suka kai wa Gwamna Nyesom Wike na jihar Rivers ba.

Atiku ya dawo

Legit.ng ta tattaro cewa shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Dr Iyorchia Ayu, da sauran masu ruwa da tsaki na jam’iyyar suna lalubo hanyoyi daban-daban domin kawo karshen rikicin kafin zaben gwamnan Osun da aka shirya gudanarwa a ranar 16 ga watan Yuli, da kuma babban zaben shekarar 2023.

Atiku wanda ake sa ran zai dawo a farkon makon nan, ana sa ran zai jagoranci zarcewa domin tabbatar da nasarar PDP a jihar.

Mataimakin Atiku ya tabbatar da faruwar lamarin

Kakakin Atiku, Paul Ibe, ya bayyana cewa Atiku zai je Osogbo ne domin jagorantar gangamin jama'ar jihar domin kada kuri'unsu ga dan takarar gwamna na jam'iyyar PDP, Sanata Ademola Adeleke.

Ibe ya ce:

"Atiku zai jagoranci jagoranci zaman sulhu don karfafawa tare da tabbatar da warware dukkan batutuwan da suka taso bayan kammala zaben fidda gwani da zaben mataimakinsa"

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN