2023: APC, Tinubu na cikin matsala yayin da dubban yan APC suka koma PDP a jihar Kebbi


Wani sabon rikici ya barke a jam’iyyar All Progressives Congress (APC), yayin da dubban ‘ya’yan jam’iyyar mai mulki a ranar Alhamis, 21 ga watan Yuli, suka sauya sheka zuwa jam’iyyar adawa ta PDP a garin Gulma da ke karkashin karamar hukumar Argungu ta jihar Kebbi. Shafin isyaku.com ya samo
.

Legit.ng ta ruwaito cewa wadanda suka sauya sheka sun samu jagorancin Alhaji Mansur Adamu Gulma Yargyra, tsohon jigo a jam’iyyar APC a jihar, inji rahoton The Nation.

Masu sauya sheka daga APC sun bada dalilai

A madadin wadanda suka sauya sheka daga jihar Kebbi, Mansur ya ce ya bar jam’iyyar APC mai mulki ne sakamakon rashin adalci da wasu masu son kai da ba su kaunar jam’iyyar a zuci suke yi wa da yawa daga cikin ‘ya’yan jam’iyyar.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN