Wata mata ‘yar Najeriya ta ja hankalin mutane kan karfin kudi na shahararren manhajar TikTok.
A cikin wani faifan bidiyo da ya samu ra'ayoyi da dama a shafukan sada zumunta, matar ta bayyana jin dadin ta game da binciken da ta yi a baya-bayan nan game da shahararriyar manhajar.
Ta bayyana cewa app din ya biya ta sau biyu bayan ta raba 'yan bidiyoyi. A cewarta, an fara biya ne a Yuro yayin da aka biya na biyu dala.
A cikin wani faifan bidiyo da @gossipmilltv ta watsa, ta nuna kudadenta na $327 (N136k), kuma ta tambayi dalilin da yasa mutane suka boye sirrin cewa manhajar tana biyan mutane kudi.
A cikin kalamanta:
"Mutane na tiktok za su canza rayuwar ku, wasu za su iya rufawa o. Kuna can, kuna tunanin tiktok na kananan yara ne. Ku zo ku ga kudin da na yi. Na farko na Euro ne. Wannan na dala ne." A cewarta.
Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun Labaran mu kai tsaye
https://chat.whatsapp.com/J8ryqryDtwR9yvxrOOBlJU
Domin zama Wakilin mu a garin kuu LATSA NAN
Domin samun Labaran mu ta Facebook LATSA facebook.com/isyakulabari sai ka Danna LIKE PAGE
Domin samun Labaran mu ta GOOGLE ka rubuta ISYAKU a GOOGLE ka danna search za ka gan isyaku.com