Majalisar Dattawan Najeriya ta amince da baki ɗaya sabbin ministoci Bakwai da shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, ya gabatar mata, kamar yadda Premium Times ta ruwaito.
Sabbin ministoin da majalisar da amince da su sun haɗa da, Henry Ikechukwu daga Abiya; Umana Umana daga Akwa Ibom; Ekumankama Nkama daga Ebonyi da Goodluck Opiah daga jihar Imo.
Sauran sune; Umar El-Yakub daga jihar Kano; Ademola Adegoroye daga jihar Ondo; da kuma Odum Udi daga jihar Ribas.