An damke wata mata mai aikata mugun aiki bayan jami'an tsaro sun aika miyagu hudu barzahu da gaggawa (Hotuna)


Jami’an rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna sun kashe ‘yan bindiga hudu a Saminaka da ke karamar hukumar Lere a jihar. 

‘Yan sandan sun kuma kwato bindigu kirar AK47 da Ak49 dauke da alburusai masu rai da kuma wata motar aiki da ‘yan fashin ke amfani da su.  

Kakakin rundunar ‘yan sandan, DSP Mohammed Jalige, wanda ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa a ranar Alhamis, 16 ga watan Yuni, ya ce farmakin ya kai ga damke wata mata da ta amsa laifin bayar da makamai da alburusai ga ‘yan bindiga a jihar.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN